. August 2018 - hausanet hausanet





Friday, 31 August 2018

HANYOYIN MALLAKAR MACE CIKIN SAUKI! 





HANYOYIN MALLAKAR MACE CIKIN SAUKI! 

Mata suna tambaya wai kowa ya tashi sai yace hanyoyin mallakar miji. 

Toh su ba'ason a mallakesune? 
Ganin haka muka ga cewar ya kamata mu danyi hobbasa ta yadda xa'a musu adalci.

Gashi yau mun sauke nauyi kowa ya daure ya karanta saboda xai karu sosai. 

Mata su karanta sbd suga hanyoyin da ake mallakansu. 

Ga kadan daga cikin hanyoyin mallakar wanda xa kaga mace ta rinka binka xai xai sai abunda kace

1)Banda kara mata wato kishiya idan ka aureta ka gama aure kenan

2)kullum ka shigo da kaji da kayan sanyi kamarsu ice cream da maltina

3)Ka rinka yi mata wanki da guga tana xaune tana hutawa

4)da safe ka mata abin karyawa ka ajiye ka tafi aiki, idan ta tashi sai ta ci ,ta sa maka albarka

5)Ka hutar da ita girki kwata kwata idan axahar tayi ka sayo mata abinci ka kai mata

6)Da dare ka dauke ta ku shiga gari shan iska daganan ku sayo kayan fruit

7) Duk weekend karinga daukanta kuna xuwa garuruwa shakatawa

8)Duk karshen wata ka kawo mata albashinka tadiba ta sammaka nasa kati a waya dana shan mai

9)Duk biki ka bata N50,000 kudin anko

10)Idan taje kasuwa ka rike mata jaka da duk abinda ta rike ta rinka tafiya dan ita sarauniyace

11)Duk lokacin da kake gida ka rika yimata abubuwan nishadi domin ka faranta mata rai ta ringa dariya 

12)Ka rinka goyata idan ta gaji da xama ko ta nemi haka

13)Idan ta nemi kamata kukan doki ko jaki ko kaxa ko bera ko kuma na yara to karinga yimata 

14)karinka shigowa gida karfe 4 ku huta kafin ku fita 

  Wadannan sune kadan daga ciki. 
A jarraba agani sai naji daga gareku!



SHARE

TRU
LOVE
NEVER
END

Yadda za a rufe kasuwar ' yan wasa ta Turai

An saye Sahin daga Borussia

Werder Bremen ta kammala sayen Nuri Sahin daga Borussia Dortmund.
Zai saka riga lamba 17 a kulob din na Jamus.

Hull City ta sayi dan wasan bayan Villa

Hull City ta sayi dan wasan bayan Aston Villa Tommy Elphick, mai shekara 30,domin ya buga
mata wasan aro na kaka daya

Nariano ya maye Ronaldo

Kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid ta bayyana dan wasanta Mariano Diaz a matsayin wanda zai cigaba da saka rigar Cristiano Ronaldo,mai lamba
bakwai.

Ina cikin wadanda suka fi iya aiki —Mourinho

Kocin Manchester United Jose Mourinho ya ce ko bai ci gasar Firimiya ba, zai kasance daya
daga cikin wadanda suka fi iya aikin horas da 'yan wasa. Mourinho ya ce shi kadai ne kocin da ya ci kofi
takwas a Italiya da Sifaniya da Ingila.

Ronaldo zai sayi kulob din La Liga

Tsohon dan wasan gaban Brazil Ronaldo zai sayi kulob din La Liga Real Valladolid ranar Litinin,
In
ji, AS.

Mourinho: Na ji dadin yadda masoya Man U
suka yi mini

Kocin Manchester United. Jose Mourinho ya ce shi ya ji matukar dadin yadda masoya kulob din
suka yi bayan kulob din ya sha kaye a Old Trafford ta hannun Tottenham.
A jawabin da ya yi wa manema labarai dazu, Mourinho ya ce masoyan Man U din sun nuna wa
kulob din goyon bayan duk da cewa ya sha kaye a gida

.Tsakanin Mo Salah ne da hukumar kwallon kafa
ta Masar

Kocin Liverpool Jurgen Klopp ya yi tsokaci kan matsalar Mo Salah da hukumar kwallon kafa ta
Masar: "Game da lamarin hukumar kwallon kafa ta Masar ba zan iya magana da yawa ba, abu ne
tsakanin dan wasan da hukumar kwallon kafar. Na yi magana da Mo game da shi. Ba mu da
hurumin tsoma baki a lamarin. Za su warware matsalar, na yi imanin hakan"

Liverpool za ta dauki koci kan 'throw-ing'

Kocin Liverpool Jurgen Klopp yana magana game da daukar kwararre kan wurga kwallo (wato throw-ing),Thomas Gronnemark. Klopp ya ce Gronnemark ne ya fi iya wurga
kwallo a wasan kwallon kafa. Ya kuke ganin wannan matakin da kocin Liverpool ke son daukawa?

Da wa Chelsea za ta fafata a gasar Europa?

Arsenal tana rukuni na E tare da Sporting Lisbon (ta Portugal) da Qarabag (Azebeijan) da kuma
Vorskla (ta Ukraine) Chelsea tana rukuni na L tare da PAOK (ta
Girka) da kuma Borisov (ta Belarus) da kuma Vidi (ta Hungary) Celtic tana cikin rukuni na B tare da Salzburg (ta Australiya) da Leipzig (ta Jamus) da kuma Rosenborg (ta Norway)

Ina Luka Modric ke son zuwa?

Dan wasan tsakiyar Croatia Luka Modric, mai aashekara 32, ya ce yana son cigaba da zama a
Real Madrid "na tsawon shekaru masu yawa nan
gaba ," yayin da shugaban kulob din, Florentino
Perez, ya ce Inter Milan ta so "ta ki biyan
komai" a zawarcin da ta yi wa dan wasan a
lokacin bazara, in ji Football Italia .
12:33

A wane rukuni Arsenal za ta buga a gasar
Europa?

FC Salzburg za ta kasance a rukunin B. Ita kuwa
Zenit St Petersburg za ta taka leda ne a rukunin
C. Anderlecht tana rukunin D yayin da Arsenal ke
ruykunin E. Olympiakos tana rukunin F. Ita kuwa
Villarreal tana G. An ambato Lazio a rukunin
H.An saka Besiktas a a rukunin I. Sevilla kuma
za ta shiga J. Dynamo Kiev za ta fafata a
rukunin K.
12:28

Ana fitar da jadawalin gasar Europa
Yanzu haka an fara fitar da jadawalin gasar
Europa. Bayer Leverkusen za ta kasance a
rukuni na A.
12:08
PSG na son kammala sayen dan Kamaru
Zakarar gasar Faransa Paris St-Germain tana
fatan ganin ta kammala yarjejeniyar sayen dan
wasan gaban Stoke City da Kamaru mai shekara
29, Maxim Choupo-Moting, in ji Mail.
12:03

Wane dan wasa ne zai bar Liverpool a yau?
Ta yiwu Lazar Markovic zai kasance dan wasa
daya tilo da zai bar Liverpool a yau, kamar yadda
Liverpool Echo ta ruwaito.
Jaridar ta ce dan kasar Serbiya din mai shekara
24 yana da zabi tsakanin kungiyar PAOK ta Girka
da kuma kungiyar Anderlecht ta Belgium.
Dan wasan gefen ya koma Anfield ne a lokacin
zafi na shekarar 2014, kan kudi fan miliyan 20
amma bai buga wa Reds wasa ba tun shekarar
2015, inda yi ta buga wasan aro cikin yawancin
shekaru ukun da suka gabata.
11:53

Chelsea ta ki sayen dan wasan Lyon
Chelsea ta yi watsi da damar sayen dan wasan
tsakiyar Lyon da Faransa Nabil Fekir, mai
shekara 25, a lokacin zafi, kamar yadda
shugaban kungiyar kwallon kafar ta Faransa
Jean-Michel Aulas ya fada. Liverpool dai tana
hakon Fekir, kamar yadda Mail ta ruwaito
11:46

Everton na da kwarin gwiwar rike Lookman

Everton tana da kwarin gwiwar cigaba da rike
Ademola Lookman, duk da cewar RB Leipzig,
wadda ta yarda ta biya fan miliyan 25, kan dan
wasan mai shekara 20, tana son dan wasa, in ji
Liverpool Echo

Assalamu alaikum
Jama'a barkanku da zuwa wannan shafin da za
mu kawo muku labarai game da yadda za a rufe
kasuwar musayar 'yan wasa ta Turai

ZAFAFAM HOTUNAN MA AURATA

NI BA KALAR MATAN DA KUDI KE RUDA BANE- Inji Jaruma rahama sadau



ta zargi wani mutum da kokarin amfani da kudi wajen kaiwa gareta kuma ta jaddada mana da ma dukkan masu irin wannan kudirinta na  cewata daga cikin matan da kudi yake tasiri akan bane
su.

Zaki yayi masa rungumar soyayya

M


Zakin ya rungumin mutum ne bayan da ya kawa masa ziyara a gidaa ajiye namun daji dake kasar Mexico bayan tsawon lokaci da ba su hadu ba.








Rahotanni sun nuna cewa mutum ne ya ceci
zakin daga wani mawuyacin hali, inda daga
bisani ya kawo shi gidan namun dajin, wanda
hakan ya sa suka saba da juna.

Thursday, 30 August 2018

WAYYO CIKINA

WAYYO CIKINA
Wani Mai Gida Ne Yaji Sanarwar Duk Wanda Yake D Yara 5 Xa A Qara Albashinsa Yakai Dubu Dari Sai Mai Gidan Nan Ya Cewa Matarsa Kinga Dama Inada Da Guda 1 Tare Da Wata Budurwata Amma Gudun Bacin Ranki...........

Yasa Ban Gaya Maki Ba To Yanxu Inaso Inje In Karbo Dana Daga Wurin Ta Kinga Saimu Hada Da "Ya"Yanmu Guda 4 Kinga Sun Cika Biyar Kenan Matar Dai Bata Ce Uffan B Mai Gida

Ya Dauki Hula Y Fita Koda Gogan Ya Dawo Da Shegen Dansa Sai Y Tarar Saura Guda 1 Mai Gida Ya Tambayi Matarsa Ina Sauran 3 Matar Tace Ashe Bakai Kadai Kaji Sanarwar Ba Suma Babansu Yaxo Y Tafi Dasu

Modric ya lashe kyautar gwarzon dan wasan Turai

Hukumar kwallon kafar Turai UEFA ta mika kyautar gwarzon dan wasan shekara na nahiyar ga Luka Modric dan wasan kasar Crotia da ke

taka leda a kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid yau a Monaco bayan rawar da ya taka a kakar wasan da ta gabata. Bayan karbar lambar yabon Modric, ya yaba da irin dawainiyar da ya ce mahaifinsa ya yi masa

wanda shi ne ya jajirce tare da bashi kwarin gwiwar ganin ya kai matsayin da ya ke yanzu. Modric wanda ya tallafawa Club dinsa wajen
lashe kofin zakarun Turai karo na 3 a jere ya

kuma yi rawar gani a gasar cin kofin duniya inda ya kusa kai kasar ta sag a nasarar lashe kofin duniya kafin faransa ta yi waje da su.

Modric mai shekaru 32 ya ce ya yi matukar alfahari da lambar yabon tare da mika godiya ga
ilahirin wadanda suka horar da shi tamaula a gida da kuma a bangaren kungiyoyi. Luka wanda ya faro

kwallonshi da Club din Dinamo Zagreb kafin kulla kwantiragin shekaru 4 da Tottenham daga bisani kuma Real Madrid
ta saye shi kusan shekaru 6 da suka gabata

UEFA Champion league ta fitar da jadawalin gasar zakarun Turai na bana

Hukumar kwallon kafar Turai UEFA ta fitar da jadawalin kungiyoyi 32 da za su fafata a gasar lashe kofin zakarun Turai, inda ta rarraba su
zuwa rukuni 8

Rukunin farko na jadawalin, wato rukuni A ya kunshi kungiyoyi irinsu

Atletico Madrid da Dortmund da Monaco da Club Brugge.

Sai kuma rukunin B da ya kunshi Barcelona da TOTTENHAM da PSV da kuma Inter Milan

Akwai kuma rukunin C da ya kunshi PSG da Napoli da LIVERPOOL da kuma Red Star Belgrade.

Yayinda rukunin D ya kunshi kungiyoyi irinsu Lokomotiv Moscow da Porto da Schalke da kuma Galatasararay

Akwai kuma rukunin E daya kunshi Bayern Munich da Benfica da Ajax da kuma AEK Athens

Ka zalika rukunin F ya kunshi kungiyoyi irinsu MAN CITY da Shakhtar da Lyon da kuma Hoffenheim

Rukunin G kuma akwai mai rike da kambu Real Madrid da Roma da CSKA Moscow da Viktoria Plzen

Yayinda rukunin H kuma ya kunshi Juventus da MAN UTD da Valencia da kuma Young Boys.

YAUCHE RANAR NUNA SOYAYYA


YAU CE RANAR NUNA SOYAYYA
Anaso duk wani masoyi ya dora hoton masoyiyarasa/masoyinta a dp hadi da zafafan kalamankauna so ake yayi 




24hrs.Yau ne zamu gane masu yaudara,wadanda basu da budurwa/saurayi dayaDuk wanda ka tura mawa bai dora ba to ka tabbatar da mayaudari ne ko mayaudariyaceehee Ki dora ynzu ina kallonka/ki aha nidai ga NASA 

YAR BIRNI KO YA QAUYE Part -1

YAR QAUYE KO 'YAR BIRNI PART 1
Na Rahamat Muh'md Rufa'i Nalele
Bismillahirrahamanur-rahim Part 1

0818 152 1679
Misalin qarfe 1:30am nadare ya tashi dan yin sallar dare wato lafula.
Bayan yayi alwa'la Zaiyi sallar kenan yaji kukan yarinya Abin yabashi mamaki Kamar zae share amma dae. Yafasa yabude kofar ahankali yana nazarin tsakar gidan Yayah me zaka kayi awaje Yaji qalinsa Amar yafa'di hakan Yace naji kukan wata yarinya ne saurara kaji Canko shima yaji kukan yarinyar yace plx yayah
karka tafi gunta dan Allah. kasanifa bamusan kan qauyan nanba plx don't leave Yace no brother bazan iyaba in fitaba inajin Kukanta har cikin zuciyata........

Bae jira cewar Amar ba yafita
Ga mamakinsa sae ya dinga jin kukan sosae Tsayawa yayi cak ya tattara nutsuwar shi dan tantance inda kukan yafi fitowa Kofar gidan yanufa yabu'de Ikwan Allah Wata yarinya ya gani durkushe bata hucce 10 years ba ya haskata da wayarshi
Sam baiji tsoron komae Ba ya nufeta
Yace keee mekikeyi anan tayi shuru
Yaqara tambayarta nanma shuru tayi. Abinfa ya bashi haushi ya daka mata tsawa Ba magana nake miki bah Aburkice tatashi tana cewa um am dan Allah.......

karka daken wlhi zan gayama Yace ina jinki Tace baba Larai ce tace saita kasheni inhar ban kawo mata kudintaba Kuma wlhi Iniya ne 'dan hansae ya bugemin farantin Yace farantin me Tace farantin tallan duk goran yazube akwata shine naje nagaya mata wae batasan zancan ba innemo mata ku'dinta. Kuma naje gan hansae tace ko asi bata maganinta bare nera talatin da
biyar Shine dana koma nagaya mata tace wlhi kudinta zanne momata kota kasheni Yace tun yanshe abin yafaru tace tun mangariba,,,,,,,,,,,

yace shine baki koma gidaba har yanzu tace To ai idan nakoma zata kashenin. dan ina kalla isma'ila 'dazo yazo nemana. Shine na6oyema
ganinsa Zamu ci gaba kukasance damu Dan kawo muku cigabansa
www.hausanet.ml zamuci gobe in Allah ya kaimu
Amin

Wednesday, 29 August 2018

Yadda Ta Kaya A Gasar Neman Tikitin Shiga Wasannin Champions League

 Dan kwallon Barcelona, Paco Alcacer 
ya koma Borussia Dortmund, a matsayin aro zuwa karshen kakar wasannin bana. Dan wasan mai shekarun 24 ya zo kungiyar Barcelona ne daga Valencia a shekarar 2016 kan kudi Euro miliyan 30 kimanin (£27.3m) amma ya kasa shiga cikin manyan

‘yan wasan kungiyar Barcelona.
Dortmund ta ce suna da ra'ayin sayen Alcacer kan kudi Euro miliyan 25 (£ 22.7m) a karshen kakar wasan bana, kungiyar Real Madrid ta ce
tana sha'awar sayen dan wasan gaba na Manchester City, Raheem Sterling, mai shekaru 23, a duniya amma sai kakar wasa mai zuwa

Har ila yau Real madrid tana bukatar sake dawo da Mariano Diaz daga Lyon ta hanyar kudin dalilin da suka kai yuro Miliyan 22 kimanin fan miliyan (£ 19.9m) sai dai Sevilla, zata amince da farashin  Miliyon 35m (£31.8m kan sayar da dan wasan.
Barcelona, na son sayen dan wasan tsakiya

kafin a rufe saye da sayarwar ‘yan wasa a ranar Laraba, amma kulob din ya yanke shawarar sayen dan wasan Manchester United Paul Pogba, mai shekaru 25 da haihuwa. Dan wasan gaba na Arsenal Alexandre Lacazette na Faransa, mai shekaru 27, da haihuwa yana duba
makomarsa a Emirates.

Dan wasan Tottenham mai shekaru 28 da haihuwa Danny Rose, zai ki amincewa da yarjejeniyar komawa kungiyar Paris St-Germain a matsayin aro. Tsohon dan wasan Brazil da Real Madrid Ronaldo na shirin sayen kungiyar kwallon kafa ta Valladolid dake kasar Spain. Real Betis, tana shirin daukar dan wasan dan kasar Brazil Rafinha mai shekaru 25, da haihuwa a matsayin aro daga kungiyar Barcelona.

Dan kwallon Liverpool Sheyi Ojo, mai
shekaru 21, a duniya na shirin komawa kungiyar Stade de Reims na Faransa a matsayin aro har
zuwa karshen kakar wasan bana bayan da dan wasan ya ce yana sha'awar komawa Ligue 1na
kasar faransa. Tsohon dan wasan Manchester City Yaya Toure, mai shekaru 35, a duniya yana kusa da
shiga wani sabon kulob bayan da tsohon dan dan wasan Ivory Coast, ya yi gwajin lafiyarsa a London.
Fenerbahce ta musanta rahotanni da suke cewa tana kokarin shiga cikin sayen dan kwallon Tottenham Moussa Sissoko, mai shekaru 29.

Dan wasan Barcelona Gerard Pique, mai shekaru 31, da haihuwa ya ce ba shi da sha'awar komawa kungiyar Manchester United, da ke taka leda, dan wasan dai ya bar Old Trafford zuwa Nou Camp, a shekarar 2008

LABARIN WASU MASOYA


Labarin wasu masoya ne zan baku da fatar zaku fahimce ni. Sudai wadannan masoya sun kasance
daga farkon soyayyar su,kamar ‘yan biyu ne koda yaushe suna tare,suna fadawa juna maganganun soyayya har ma da dariya,basu son abinda zai sosa ran daya.soyayya tayi karfi sosai har alkawarin aure ya shiga

tsakaninsu,saboda sun yarda da
junansu fiye da kima.To shidai yaron
dan talakawa ne.Gidansu ba masu wadata bane,amma duk da haka ta
nuna ta amince dashi,ya kamu da
kaunarta kauna mai tsanani.Ana cikin haka sai chanji ya shiga.masu kudi da manyan motoci suka fara farautarta kuma wani daga cikin
ya samu amincewarta,dan shi babban dan kasuwa ne kuma ya nada kudi.Ya aureta yakai gidansa.
Allah SWA ya arzuta ta da juna biyu
har ya kai wata ukku,sai ya fara jin ya gaji da ita,karshe dai ya sake ta saki

3 ta koma gidansu tana kokawa da
kannenta wajan cin abinci,rayuwarta ta lalace..Shi kuma tsohon saurayin nata Allah.ya bashi wadata bayan
ta auri mai kudi,shi kuma duk da yana talaka sai wani attajiri ya bashi ‘yarsa,kuma tafi ta kyau.wannan kenan,Dan Allah mu kiyaye maza da mata mu daina sanya kwadayi cikin
harkar aure dan gudun afkawa cikin
wahala.

An kama wasu matasa 2 suna luwaɗi a makabartar jahar Kano

Allah ya tona asirin wasu matasa yan luwadi a jihar Kano, yayin da aka kama suna turmi da tabarya suna aikata badala a cikin wata. makabarta cikin birnin Kano kamar yadda rahotanni suka tabbatar. NAIJ.com ta ruwaito wannan lamari ya faru ne a ranar Litinin data gabata na watan Agusta, inda wasu matasa a karamar hukumar Gwale suka kama yan luwadin a lokacin da suke tsaka da tafka wannan mummunan laifi Wannan lamari yayi matukar bata ma mutannen wannan unguwa rai, inda suka fusata suka yi ma yan luwadin

dukan kawo wuka, suka kusan kashesu, da kyar da sudin goshi Yansanda suka kwacesu. Kaakakin rundunar Yansandan jahar
Kano, Magaji Musa Majia ya  tabbatar da.faruwar lamarin, inda yace a yanzu haka matasan suna hannunsu, kuma.bincike ya kankama zuwa yanzu..Jama’a da dama a jihar Kano sun koka da karuwar matasa masu shiga.mummunan dabi’ar nan ta luwadi inda.namiji ke neman namiji, da madigo.inda mace ke bin mace don samun.biyan bukata, sai dai yawancin jama’an.sun danganta lamarin ga illolin shaye.shaye.

MATASHI lukman - banban buri a duniya na hadu da hadiza gabon

amar Yadda Hausawa Kance Kowa Da Abunda Ya Dameshi Haka Kuma Kowa Da Masoyinshi, Lallaikam Wannan Batu Haka Yake. Na Samu Damar Zantawa Da Wani Matashi Dan Asalin Jahar Naija Wanda

Yanzu Haka Yana Zaune Garin Kano
Tsawon Shekaru Hudu Domin Kawai
Allah Ya Hadashi Da Daya Daga Cikin Fittun Jaruman Masna’antar
Kannywood, Wato Jaruma Hadiza Aliyu Gabon, Wakilinmu Auwal M Kura Ya Samu Damar Tattaunawa Da Wannan Matashi Mai Kimanin Shekaru 23 A Duniya Mai Suna Lukuman

Wanda Akeyi Masa Take
Da (Na Gabon) Ga Kadan Daga Cikin Yadda Tattaunawa Tasu Ta Kasance:vAuwal M.kura: A Takaice Zanso Sanin Sunanka da Kuma Takai Tattacen Bayani
A kanka? Lukman: Sunana Lukman Amma Amfi Kirana da Na Gabon, Yan Zu Haka Inada Kimanin Shekaru 22 zuwa Da Uku Sannan Ni Haifaffan Garin Naija Ne, Kuma Nazo Jahar Kano Tsawon Shekaru Hudu Ke Nan .

Auwal M.kura: Mai Ya Kawo Jahar
Kano? Lukman : Toh Babban MaKasudin Zuwana Kano Tun 2014 Shine,Nazo ne Domin Na Hadu Da Hadiza Aliyu Gabon, Auwal M.kura: Toh Tsawon Wannan Shekaru Ko Kasamu Damar Ganin Ita Hadiza Gabon Din ? Lukman: Gaskiya Aa
Auwal M. Kura: Bakabi Hanyoyin Da
Kasan Zaka Ganta Bane ?

Lukman: A Tsawon Wadannan Shekaru Kullum Cikin Bin Duk Wata Hanya Da Zaisa Ko Sau Daya Na Ganta ne , Amma Haryana  Bamu Hadu Ba,Akwai Gurare Da Yawa Wanda Har Kudi Sukan Amsa A
Gurina Da Sunan Zasu Hadani Da Ita
Amma Daga Baya Bazasu Hadani Da Ita Ba, Numbobin Waya kam Inada Sama Da Guda Ashirin Wanda Duk Sai Nabiya Ake Bani Ana Cemin Ta Hadiza Gabon Ce Daga Baya Koda Nakira Sai Wani Can Daban Zanji Ya Dauka , Auwal M kura: Toh Ganin Yadda Ka
Fuskanci Wadanan Kalubale, Kuma Baka Cimma Muradinka Na Ganin Abar Began Taka Ba , Wato Hadiza Gabon, Baisa Kaji Ka Hakura Ba?

Lukman: Kokadan Illa Kara Samun
Karfin Gwaiwa Danayi, Domin Kuwa
Yanzu Haka Nayi Mata Wakoki Da dama Ko Allah Zaisa Wakar Taje Gareta,

Auwal m.kura: Mai Yasa Duk Sauran
Jaruman Hausa Film Nan, Kai KazabivHadiza Gabon?
Lukman: Ni Dai Kawai Ita Allah Ya
Samun Naji Tana Burgeni , Kuma Ina
Matukar Girmamata Saboda Mace Mai Tausayi Da Kamala,
A Karshe Wani Kira Zakayi Da Ita
Wannan Jarumar Da Kuma Hanyar Da Zata Sameka Koda Ta Ga Wannan Fira Da Mukayi Da Kai Don Ganin Kun Hadu Da Juna?
Lukman: Toh Ni Yanzu Ina Zaune A
Kano ne, Amma Idan Allah Yasa
Wannan Sako Ya Isheta , To ina
ronkanta Data Cika Burin Na Haduwa Da Ita, Domin Kuwa Burina A Duniya Shine Naga Na Hadu Da Hadiza Aliyu Gabon, Ta Hanyar Tuntbarka Dan Jarida(Auwal M Kura) Ko Gidan Jaridu Koda Jaruma Hadiza Aliyu Gabon Ta Gamu Da

Wannan Sako Zata Iyya Tuntunbar Gidajen Jaridu Kamar Haka: Jaridar Tarayya Mikiya Rariya  Ko Kuma Matashin Dan Jarida #Auwal M Kura A Number Kamar Haka :
0818 152 1679

An zabi kwallon Ronaldo a matsayin wanda ta fi kyau UEFA CHAMPION LEAGUE

An zabi kwallon Ronaldo a matsayin wanda ta fi kyau a bana A bana ne Cristiano Ronaldo ya ci Juventus wata kwallo da ta ba jama’a mamaki inda yayi tsalle ya watse ta baya har cikin ragar Gianluigi Buffon. Wannan kwallo aka zaba a matsayin

wanda ta fi kowace kwallo kyau a 2018..Sama da mutane 200, 000 cikin mutane.346, 915 da su ka shiga shafin UEFA su ka zabi kwallon da tsohon ‘Dan wasan Real Madrid Ronaldo a Turai. A bara ma dai ‘Dan wasan Juventus Mario Mandžukić ne ya lashe kyautar 

Karin bayani

Ronaldo ya ci Juventus a Gasar Zakarun Nahiyar ne lokacin yana bugawa Real Madrid. Kwallon ‘Dan wasan Marseille Dimitri Payet ce ta zo na biyu yayin da kwallon da Eva Navarro ta ci a wasan Sifen da Kasar Jamus ta zo 3. Kwanan nan kun ji

cewa Gwarzon ‘Dan wasan Duniya Cristiano Ronaldo ya bayyana cewa tafin da Magoya bayan Juventus su ka yi masa a lokacin da ya zura kwallo a ragar su ce ta sa ya koma taka leda a Kungiyar a shekarar nan

Tarar aradu da ka: wasu Matasan jihar Benuwe sun ɗana ma Sojoji tarko, sun kashe Soja 1

A ranar Lahadi ne wasu matasan kabilar Tibi na jihar Benuwe suka sake kashe wani jami’in rundunar mayakan Sojan kasa a jihar Benuwe, kamar yadda jaridar Daily Trust ta

ruwaito Premium Times ta ruwaito matasan sun kashe jami’in Sojan ne yayin da yake tafiya tare da wani abokinsa akan babur da misalin karfe 2 na rana, inda suka shirya masa tarkon rago, kuma ya.fada, a kauyen Gbeji dake cikinkaramar hukumar Logo

Tuesday, 28 August 2018

Gerard Pique Ya Ce Zai Yi Kyau Paul Pogba Ya Koma Nou Camp

Dan wasan baya na
Barcelona mai suna Gerard Pique, mai shekaru 31, ya ce "zai yi kyau idan dan wasan Manchester United, Paul Pogba

mai shekaru 25, ya koma Nou Camp a nan gaba. Dan wasan Chelsea da Ingila Gary Cahill, mai shekaru 32, ya ƙuduri aniyar cigaba da zama a
kulob dinsa na Chelsea duk da yake fama da rashin shiga tawagar Kocin kungiyar Maurizio Sarri

Tsohon dan wasan Arsenal d Thierry Henry, mai shekaru 41, na duba yuwuwar zama a kungiyar Bordeaux a matsayin kocinta saboda tsoron
rashin kudi a kulob din. Matashin dan wasan baya na West Ham,

mai suna Reece Oxford, mai shekaru 19, yana shirin komawa kungiyar Eibar na kasar Spain a matsayin aro inda suke son biyan kudi fan miliyan 1.8

Eden Hazard Ya Ce Zai Koma Real Madrid Saboda Zinedine Zidane

Dan wasan Roma da Netherlands Kevin Strootman, mai shekaru 28, ya yanke shawarar kammala shekaru biyar a Serie A ta hanyar komawa Faransa don shiga Marseille kan kudi fan miliyan £ 22.6m.

Tsohon dan wasan tsakiya na Chelsea kuma
dan wasan Brazil Ramires, mai shekaru 31, yana kusa da sake shiga Benfica a kan aro daga Jiangsu Suning ta kasar Sin. Paris St-Germain

sun yi watsi da "hasashe da
ake danganta su da dan wasan Tottenham da Denmark dan wasan tsakiya mai suna Christian Eriksen, mai shekaru 26, a duniya. Manchester United, sunki amincewa game da zawarcin da kungiyar AC Milan da kuma Atletico Madrid suke yi domin sayen Martiard Anthony mai shekaru 22 da haihuwa. Dan
wasan mai tsaron gida na Belguim da Liverpool Simon Mignolet ba zai bar Liverpool kafin karshen saye da sayarwa na kakar wasa ta.Turai ta ban aba, dan wasan mai shekaru 30 na da damar samun kansa a cikin ‘yan wasan farko a kungiyar.
Arsenal na kan gaba wajan kulla yarjejeniya

tare da kamfanin Adidas, na tallafin kudi fam miliyan £300m kasancewar kwangilarta da Puma da ta kare a karshen kakar wasa ta bana

SAKONNIN SOYAYYA


Kin wadata zuciyata da farin-ciki,
kin haskaka rayuwata da haskenki, kulawarki a gare ni ta musamman ce, hakan ya sa
nake jin kaina tamkar sarkin wata
masarauta mafi girma da
karfin iko. Ina Son Ki


2 Ke ce kaddarar da na jima ina
tsimayin tarar da ita a
rayuwata, zan kasance a duk inda
kike, zan tsaya a duk inda
kika tsayar da ni. Ina son ki, adadin
son da kalmomi ba zasu
iya siffantawa ba


3 Ina jin labarin soyayya ne a da,
tamkar tatsuniya, amma a
yanzu bayan na haɗu da ke, na
gaskata soyayya wata aba ce
wadda ke da tasirin sanya farin-ciki a
cikin zuciya. Ina fatan
zaki kasance tare da ni, domin zama
maganin damuwata na
tsawon rayuwa? Ina Son Ki


4 Koda a ce zaki sa wuta a jikina na
babbake na zama toka,
ba zan damu ba, matukar zaki ɗauke
ni, ki kasance tare da ni
a duk inda kike. Fatana mu kasance
tare da juna a cikin wuya
ko daɗi. Ina Son Ki


5 Son da nake yi miki, tamkar ruwan
lemo ne da ke rufe a
cikin kwalba, irin wanda babu irin sa
ko makamancin sa a faɗin
wannan duniyar. Ina fatan zaki karɓa
domin jin irin ɗanɗanon
da ke kunshe a cikinsa? Ina son ki.
6 Ina fatan Allah Ya bar mu tare, cikin
aminci da kaunar juna


7 Tun ranar da na fara ganin ki, na ji
a jikina, watarana
hannuwanki zasu zamo masharin
hawayena, kuma zasu
kasance rike da ni na tsawon rayuwa,
zuciyarki zata zamo
makwancina na har abada. Na gode da
irin kulawar da kike
nuna min a kullum. Ina Son Ki Sosai


8 Kin zamo cikin baitukan wakar da
zuciyata ke rerawa a
kullum, waɗanda a dukkan lokacin da
na ji su, na kan ji dukkan
damuwata na gushewa. Tabbas ina jin
na kamu da son ki
ne kai babu ko shakka matsanancin
son ki ya shiga
zuciyata. Ina son ki ina kuma fatan
zaki amince da ni a
matsayin masoyi na hakika?


9 So tamkar wutar murhu ne da ke ci
a cikin zuciyar masoya.
Tini zuciyata ta babbake da son ki
abar tinanina. Ina son ki, so
mara misaltuwa


10 Ba zan taɓa mantawa da wannan
ranar ba, wadda dare ya
yi na kasa bacci a cikinta, saboda
tsabar tinaninki, wato ranar
da na fara ganin ki. Na Yi Kewar Ki.
11 Idan har ba kya jin irin yadda nake
ji a kan ki a yanzu, to
tabbas na san zaki ji irin hakan bayan
na mace


12 Babu wani sinadari da zai iya
mayar da zuciya, ya haɗe ta
guri guda, ta dawo da aiki kamar
yadda take a da, bayan ta
fashe ta targwatse. A saboda haka
nake rokon, da ki kasance
cikin ba wa zuciyata tsaro, karda ta yi
fashewar da za a rasa ni
gabaɗaya. Ina Son Ki


13} Ke kaɗai ce nake gani kullum a
cikin baccina, ke ce abar
begena kuma ke ce wadda nake so,
domin a gurin ki nake
tsammanin samun farin-cikin da nake
fata. Ina Son Ki


14 A wasu lokuta so yana zama wani
abu mara tausayi ga duk
wanda ya raɓe shi, ya raba mutum da
duk abun da yake da shi
na farin-cikin rayuwa, amma ni na yi
sa'a kuma na tsallake wa
sharrinsa tunda na same ki


15 A dukkan lokacin da tinaninki ya
bujuro a cikin zuciyata, na
kan tina irin yadda son ki ya zamo
abu mai matukar
muhimmanci a rayuwata. Ke ce wadda
nake so, kuma nake
fatan na rayu tare da ita, rayuwa ta
har abada


16 Za ki fahimci ma'anar soyayya, da
kuma irin muhimmancin
girman son da nake nuna miki, a
lokacin da aka ce na mutu ba
na raye. Har Yanzu Ni Dai Ina Son Ki


17 A kullum zuciyata kan nutsu ta yi
tinani, domin tsara sakon
da zan aikewa da abar tinanina a dare
ko rana, domin ganin
yalwatuwar murmushi a saman
fuskarta. Ina fatan sakonnin
nawa suna yin tasirin sanya ki farin-
ciki? Ina Son Ki


18} dukkan lokacin da masoyi ya rabu
da abar kaunarsa, ya
kan tsinci kan sa cikin kaɗaici da
damuwa na tsawon lokaci,
ya kan tsinci kan sa cikin rashin
yarda da gujewa amincewa
sauran mata. Ki kasance tare da ni na
tsawon rayuwa, karda ki
bari zuciyata ta ɗanɗani raɗaɗin
zafin rabuwa da abar so. Ina
Son Ki


19 So shi ne abu mafi tasirin warkar
da kowane irin ciwo a
cikin zuciya, kuma shi ke sanya mu jin
kanmu a matsayin wasu
mutane na musamman, a dukkan
lokacin da muke tare. Na Yi
Kewar Ki


20 Shigowar ki cikin rayuwata, gami
da irin tsantsar son da
kike nuna min, sun zama dalilan yin
murmushina a kowane
lokaci. Ba ni da wata da nake so sama
da ke. Ke ce karfina, ke
ce karsashina. Ina Son Ki


NA MATA


1 Kowace soyayya da kake gani, tana
samuwa ne a bisa wasu
dalilai, saboda haka, ina son bayyana
maka cewa, ina son ka
ne saboda, kai ne da ma wanda
zuciyata ta daɗe tana jira. Ina
tare da kai a duk inda na shiga. Ina
Son Ka


2 Matsayinka a gare ni, tamkar na
wani dutse ne na
musamman da yake jikin wani zobe,
wanda ya kasance a
dukkan lokacin da babu shi, zoben zai
zamo mummuna mara
daraja abar nunawa. Ka kasance tare
da ni masoyina. Ina son
ka, so mara misaltuwa


3 A lokacin da ka shigo cikin
rayuwata, na ji tsoron kar ka
raunata zuciyata, amma yanzu da na
same ka, ina jin fargabar
rasa ka. Ina fatan zuwan ranar da zan
zamo mata a gare ka.
Ina Son Ka

4 Ina son kasancewa ne tare da wanda
zai kasance cikin saka
ni farin-ciki, ya sa ni murmushi a
lokacin da nake cikin
damuwa, wanda zai kasance cikin so
na a kowane irin yanayi.
Na san babu wanda zai iya hakan sai
kai, a saboda haka nake
kara bayyana maka cewa, ina son ka


5 Ina fatan zuciyata da taka su narke
su zama abu guda, har
zuwa karshen rayuwa. Zan kasance
cikin yi maka addu'ar
samun nasara a dukkan al'amuranka,
kuma zan kasance cikin
son ka har karshen rayuwata


6 Kai ne ke bayyana kullum a cikin
baccina, ta cikin mafarkin
da nake fatan ya zamo gaskiya
watarana. Ina son ka, irin son
da ke kawar da zuciya daga yin
tinanin kowa face naka


7 Na yi kewar ka sosai. Na kan yi
tinanin lokacin da muke
shafewa tare, mu yi raha tare da
farin-ciki a cikinsa. Wannan
tini ne na abun da ya faru tsakanina
da kai a dangane da
soyayyarmu, ko zai sa ka tino da ni.
Na yi rashin ka a kusa da
ni

8}Zan so mu kasance tare a matsayin
miji da mata, ka
tarairaye ni ka nuna min irin yadda
kake ji na a cikin zuciyarka
a zahiri. Ni wannan shi ne kaɗai abun
da nake muradi. Ina Son
Ka

9 Idan har da a ce wasu zasu tambaye
ni wanda nake fatan
na aura, amsar ba zata wuce kai ba,
domin kai ne wanda
zuciya ke fatan ta kasance tare da shi
har abada.

10 Wanda nake fatan na aura, mutum
ne na musamman mai
baiwa ta musamman a cikin
dubunnan samari, shi ne wanda
zan iya kasancewa tare da shi a cikin
wuya ko daɗi, domin na
san tinaninsa a kullum, bai wuce
neman hanyar da zai inganta
rayuwata ba. Ina Son Ka.
LURA


A kiyaye hakkin mallaka, a guje wa
satar fasaha.
Kana da damar tura wa abokiyar
tsinkar furenka,
amma ba a amince wani ya yi amfani
da shi da
niyyar yaudarar wata ruhi ba. Akwai
Mai ganin ka/ki a ko'ina

Za'a tantance gwarzon UEFA tsakanin Ronaldo Salah, da Modric

Yan wasan sun hada da Luka Modrić, Cristiano Ronaldo da kuma Muhammad Salah.bA ranar 30 ga watan Agusta da muke cikivhukumar ta UEFA za ta bayyana wanda zai
lashe kyautar ta gwarzon dan wasan kwallon kafar a nahiya Turai. A ranar 31 ga watan Agustan ne kuma

hukumar ta UEFA za ta bayyana gwarzon dan wasanta na nahiyar turai a bangaren gasar Europa a kakarwasan da ta gabata

Taron karrama ‘yan wasan dai zai gudana ne a birin Monaco da ke kasar Faransa. Sauran ‘yan wasa 10 da hukukmar UEFA ta zabo da fari sun hada da, Antione Griezman na
kungiyar Atletico Madrid Lionel Messi na Barcelona, Kylian Mbappe na PSG da Kevin De Bruyne na Manchester City.v‘Yan wasan da ke a matsayi na 8, 9 da kuma 10bsun hada da Raphael Varane na Real Madrid, Eden Hazard na Chelsea da kuma Sergio Ramos

Sharuddan da hukumar da UEFA ke yin amfani da su wajen zabar gwarzon dan wasanta dai sun hada da bajintar da ya nuna a baki dayan
wasannin da ya fafata a matakin kasarsa nahiya da kuma matakin kasa da kasa

Monday, 27 August 2018

(BIDIYO) Yadda wasu masoya suka kwashi 'yan kallo a jami'ar Bayero ta garin Kano

Wani faifan bidiyo da yayi ta yawo a
kafafen sadarwar zamani da kuma ya dauki hankalin jama'a da dama
musamman ma a arewacin Najeriya nadauke ne da yadda wani soja ya nunawa budurwar sa kauna a gaban

jama'a a jami'ar Kano. Bidiyon dai ya nuna sojan sanye da kakin sa da ake kyautata zaton soyayya suke da budurwar ya durkusa a gaban ta yana rokon ta amince da soyayyar sa. Soyayya ruwan zuma: Yadda wasu masoya suka kwashi 'yan kallo a jami'ar Bayero ta garin Kano
(Bidiyo) NAIJ.com ta samu cewa saurayin a cikin wani irin salo na koyi da turawa, ya fiddo zobe daga aljihun sa inda ya

kuma bukaci budurwa da ta mika
hannun ta domin ya saka mata.
Sai dai budurwar wacce take a cikin
shiga ta hausawa sanye da doguwar riga da kuma jan gyale ta fashe da kukan murna ne inda ta ma kasa hada ido da shi......

Yanda Zaku Sami Kyautar 20GB A Layin Airtel

Wannan Ba Wai Cheat Bane Daga
Kamfanin ne suke bada Wannan Garabasar Domin Samun Wannan Kyautar Sai Maida Layin Da kuke Amfani Dashi Zuwa Layin Airtel ...
Domin Ku Sami Wannan Garabasar Ku Sami Kowanne Irin Layi daga nan Saiku je gurin ofis din Airtel Na Kusa daku Saiku je musu kunah son Ku Maida Layinku Zuwa Airtel Shikenan Zasu Yi Muku..nAmma Ku Tabbatar Kuna Voters Card,National Id Ko Driver Licenses Daga Nan Zasu Sanar Daku Lokacin da Layinku Zai Koma Airtel Daga nan dominb Samun Wannan Garabasar ..
Idan Layin Naku Ya Koma Airtel Saiku Sa Kati Amma Fah Dole Sai Ta Bank Basa Son Ka Siya Kati Wanda akasa a dan Karamin

Littafi Suna son Kasa Katin Naka Ta Hanyar Gizo Ta Yanda Killa Numbobi Kawai Zaka Danna A Wayarka Sai Su Baka Katin Ta Hanyar Cire Kudin Ka Ta Banki Daga Nan Idan Kasa Katin #100 Zaka Sami Garabasar 2GB idan Kasa Katin #1000 Zaka Sami Garabasar 20GB Kuma Sai Yayi Kwana Talatin Kafin Ya Kare Dadin abin zaka Iya Kara yi idan Ta Kare

ALLAH YA BADA SA'A DAGA HAUSANET.ML

Zainab indomie Meyasa Rayuwar Shirin Fim Dina Ta Lalace

jarumar da aka daina yayinta,
Zainab Abdullahi da aka fi sani da Zainab Indomie ta bayyana cewa ba ta san yaya aka yi rayuwar aktin dinta ta susuce ba duk da daukakar da ta samu a masana’antar fina-
finan Hausa Jarumar ta ce ta samu daukaka tun tana karama, amma saboda kaddara ba ta san abin da ya faru ba yanzu ta rasa komai. Ta ce, “Na samu daukaka tuna ina karama,
wani abu ya faru yanzu dai na rasa komai, babu ganganci a ciki, ba na kuma ganin laifin kowa, ban kuma zargi kowa ba sakamakon mawu yacin halin da na shiga. A halin da ake ciki ba zan iya tunawa da
komai ba, ba zan iya cewa ga abin da ya sa na samu kaina a cikin

mawuyacin hali ba Idan har laifina ne ina rokon Allah Ya yafe mini, idan ma laifin wani ne to Allah Ya yafe
masa inji ta. Jarumar ta kuma roki Allah Ya sanya ta da sauran jama’a a kan hanya madaidaiciya. Ta ce, “Na gode wa Allah saboda jarrabawar
da ya yi mini, ina rokon Allah Ya fitar da ni daga wannan jarrabawar. Na mika kaina ga hannun Ubangiji Amin summa amin

SHEDAN YANA DA WATA MATA GURGUWA

MATAR SHEDAN

SHEDAN YANA DA WATA MATA GURGUWA:

Wata rana zai wuce sai yace mata ta matsa Don bata da wani amfani, sai tai dariya Tace: "Na fi ka illah don nice nake zuwa a karshen fitsari, idan mutum yana fitsari INA rike kadan daga ciki, da ya mi'ke sai in sakar masa, ya mike ba tare da ya wanke ba!"

Sai Shedan ya bushe da dariya yace "Kin ga kuwa duk Wanda bai da tsarki baida alwala, duk kuma Wanda bai da alwala bai da sallah!" Yace lallai kuwa kin cika sheidaniya!".

MAFITA:

Ya Muslim Ummah, a duk lokacin da muke fitsari bayan mun gama mu jira kadan muyi nishi, zamu ji wani fitsari kadan mai 'dumi ya biyo baya.... WANNAN shine fitsarin da Matar Shaidan take ri'kewa don ta 6ata mana ibadanmu!!

LA'ILAHA ILLALLAH, MUHAMMADUR RASULULLAH (SAW).

Don Allah in ka karanta ka aikawa wasu don suma Su amfana, mu kuma samu tsari gabadaya daga azabar Qabari.

Allah Ya tsare mu Ameeen.

FATIHA DA SALATIL FATIHI