. UEFA Champion league ta fitar da jadawalin gasar zakarun Turai na bana - hausanet hausanet





Thursday, 30 August 2018

Home UEFA Champion league ta fitar da jadawalin gasar zakarun Turai na bana

Subscribe Our Channel


Hukumar kwallon kafar Turai UEFA ta fitar da jadawalin kungiyoyi 32 da za su fafata a gasar lashe kofin zakarun Turai, inda ta rarraba su
zuwa rukuni 8

Rukunin farko na jadawalin, wato rukuni A ya kunshi kungiyoyi irinsu

Atletico Madrid da Dortmund da Monaco da Club Brugge.

Sai kuma rukunin B da ya kunshi Barcelona da TOTTENHAM da PSV da kuma Inter Milan

Akwai kuma rukunin C da ya kunshi PSG da Napoli da LIVERPOOL da kuma Red Star Belgrade.

Yayinda rukunin D ya kunshi kungiyoyi irinsu Lokomotiv Moscow da Porto da Schalke da kuma Galatasararay

Akwai kuma rukunin E daya kunshi Bayern Munich da Benfica da Ajax da kuma AEK Athens

Ka zalika rukunin F ya kunshi kungiyoyi irinsu MAN CITY da Shakhtar da Lyon da kuma Hoffenheim

Rukunin G kuma akwai mai rike da kambu Real Madrid da Roma da CSKA Moscow da Viktoria Plzen

Yayinda rukunin H kuma ya kunshi Juventus da MAN UTD da Valencia da kuma Young Boys.