. January 2019 - hausanet hausanet





Sunday, 27 January 2019

Fati washa __Nagode maka da sani farin ciki---Fati Washa tagayawa masoyinta


Nagode maka da sani farin CikiFati Washa tagayawa masoyinta


  • Tauraruwar fina-finan Hausa da turanci, Rahama Sadau ta godewa masoyinta inda tace, Masoyi na musamman, nagode da shigowa rayuwata, Nagode da sani farin ciki Da ka yi WWW.HAUSANET.ML

Kalli wasu zafafan hotunan Rahama Sadau da abokan aikinta › Ta


Kalli kayatattun hotunan Rahama Sadau da abokan aikinta daga www.hausanet.ml




Aisha Buhari ta karyata masu cewa ta yi Allah-wadai da korar ----- Onnoghen

war gidan shugaban kasa, Aisha Buhari ta karya rahotannin da ake Yadawa na cewar ta yi Allah-wadai da Hukuncin da shugaban kasa Buhari ya Dauka na korar mai shari'a Walter Onnoghen daka mukamin Alkalin Alkalai na kasa (CJN) Mrs Buhari a cikin wata sanarwa ta Hannun Daraktanta na watsa labarai, Mr Suleiman Haruna da ya rabawa

manema labarai a ranar Asabar aBAbuja, ta bayyana wannan labarin da Ake yadawa na cewa ta yi Allah-wadai da korar Onnoghen a matsayin 'labarin kanzon kurege an ankarar da uwar gidan shugaban kasa kan wani labari da ake yadawa a Kafofin sada zumunta na zamani wanda Har ake cewa ta yi Allah-wadai da Dakatarwar da aka yiwa Walter Onnoghen, daga mukamin Alkalin Alkalai na kasa

kalli hotunan yan gudun hijirar boko haram

'Yan gudun hijirar Najeriya da ke aamun mafaka a Nijar


Rundunar sojin Najeriya ta fara kera motocin yaki (Hotuna


Rundunar sojin Najeriya a karkashin jagorancin Safsan ta, Laftanal Janar Tukur Yusuf Buratai sun soma kera motocin sulke da na yaki manya da kanana domin fuskantar abokan gaba da sauran masu Tada kayar baya a kamfanin su dake a Jihar Kaduna

Friday, 25 January 2019

Manchester City zata iya lashe kofuna 4 a wannan kaka inji Guardiola

Kocin kungiyar kwallon kafa ta Manchester City Pep Guardiola ya ce abin alfahari ne ya zamana Club din ya yi nasarar lashe kofuna har 4 cikin kaka guda dai dai lokacin da ya ke shirin Komawa wasannin cin kofin FA bayan

takaitaccen hutu. City dai ita ce kungiya daya tilo da ta ke da zarafin iya lashe kofunan Firimiya da FA da kofin League da kuma zakarun Turai la’akari da

matakin da ta ke a kowacce gasa.

Yanzu haka dai City na da tazarar maki 4 ne

kacal tsakaninta da Liverpool da ke saman

Teburi, a bangare guda kuma an ga rawar da ta

ke takawa a gasar ta FA da ma yadda ta ke

shirin tunkarar wasan karshe a gasar League

tsakaninta da Chelsea cikin watan Fabarairu

baya ga gasar zakarun Turai. A gobe asabar ne Manchester City za ta kara da Burnley a zagaye na 4 na wasannin cin

kofin FA

ka Karanta Abinda Shi'a Babban Darakta Falalu Dorayi Akan Bashar Chiroki

Allah shi yake kaddarawa bawa  samu da rashi, wanda Allah ya nufe shi da zama cikin kunci ko rashin wadatar abubuwa da saba rayuwa dasu, ba

kaskanci ba ne face jarraba da kuma

kaddarar Allah akansa.

Mai hankali yasan duniya bala'ice gida

ne na jarrabawa tsakanin wadata da

tsanani.

Ubangiji Yace;

“Kuma za mu jarraba ku da sharri da

alheri a matsayin fitina, kuma gare Mu

kuke komawa.'' (Anbiya:35). Bai

kamata ga mutum idan ya tsinci kansa

a cikin Jarrabawa ta kunci ko talauci

ko dusashewar daukaka ko ciwo ya

zargi wasu mutane ba. Allah yana

jarabtar bawa Sakamakon abin da ya

aikata ga ‘Yan uwansa mutane na

Alfahari, Dagawa da Girman kai. To

shin Ina ma matsayin takawakkali da

yadda kaddara?

Tawakkali ga Allah shine abin bukata

daga ko wane mutum,

a ko wanne hali ya tsinci kansa.

Cikakken tawakkali shin zuciya ta

nutsu ta mika komai ga Allah ta haka

za’a samu alkairi da kariyar daga

sharri.

Babu wanda ya isa ya baka daukaka ko

ya kwaceta sai Allah in dai ka dagara

ga Allah hakikani dogaro, Allah zai

azurtaka kamar yadda yake azurta

tsuntsu da sauran dabbobi.

In gaske ne mutum ya fawwala

lamuransa ga Allah, ya yadda da Allah

shi yake bada daukaka da daukewarta to sai a nisanci Kage, zargi, camfi, da

tazarta masana’antar da Allah ya baka Suna a cikin ta kai aure kai gida kasai

babur. Lallai in da kake yanzu haka

Allah ya so ya ganka

Ubangiji Yace; cikin Qurani

“Kuma Idan Allah ya shafe ka da wata Cuta, babu mai yaye ta, sai shi, idan kuma ya shafe ka da wani alheri, babu mai iya ture falalarsa. Yana samun wanda ya so daga cikin bayinsa da ita,

kuma shi mai gafara ne, mai jin kai

Portugal za ta kwace lambar yabo mafi girma da ta baiwa Ronaldo

Shugaban Portugal Marcelo Rebelo de Sousa,

ya ce gwamnatinsa tana nazari kan yiwuwar

kwace babbar lambar yabo da ta baiwa dan

wasan kasar Cristiano Ronaldo.

Matakin a cewar shugaba Rebelo de Sousa, na

da nasaba da hukuncin biyan tara da kotun

Spain ta yanke kan Ronaldo, bayan samunsa da

laifin kin biyan haraji, yayin da yake wasa a

kungiyar Real Madrid.

A shekarar 2016 Portugal ta karrama Ronaldo

da lambar yabo mafi girma da ake baiwa farar

hula ta ‘Portuguese Order of Merit’ a turance,

bayan taimakawa kasar da ya yi, wajen lashe

gasar cin kofin kasashen nahiyar Turai.

Sai dai a ranar Talatar da ta gabata, wata kotun

Spain ta yanke hukuncin tilasatawa Cristiano

Ronaldo biyan Dala miliyan 3 da dubu 57 saboda

kin biyan makudan kudade na haraji ga

gwamnatin kasar.

Da fari hukuncin kan Ronoldo na daurin

shekaru 2 biyu ne a gidan Yari amma aka

sassauta hukuncin zuwa biyan tarar euro dubu

365 na take, tare da biyan karin euro miliyan 3

da dubu 200

Amaechi ya saka ni a matsala - Buhari


A yau, Alhamis ne shugaba

Muhammadu Buhari ya ce MInistan

Sufuri, Rotimi Amaechi ya jefa shi a

cikin matsala yayin da ya yi alkawarin

gina layin dogo da za ta hade yankin

Kudu maso Gabashin kasar da Arewa.

Shugaba Buhari ya yi wannan jawabin

ne a wurin taron kaddamar da yakin

neman zabensa da akayi a cikin filin

motsa jiki na Nnamdi Azikwe da ke

garin Enugu.

Buhari ya ce abu ne mai wahala

gamsar da majalisar zartarwa na kasa

su amince da ayyukan layin dogo amma

ya ce zai yi iya kokarinsa domin ganin

'yan majalisar sun fahimci

muhimmancin gudanar da aikin.

"Amaechi ya yi muku alkawari amma

ban san yadda zan cika alkawarin ba.

Amma zanyi iya kokari na domin ganin

'yan majalisar zartarwa sun amince da

gudanar da aikin," inji Buhari.

Ya ce ba a gabatar wa Majalisar

Zartarwa alkawarin da Amaechi ya yi

ba inda ya ce zai fi dacewa a bari

Majalisar su amince da aikin kafin a

bayyana wa mutane.

Shugaban kasar ya mika godiyarsa ga

mutanen yankin bisa yadda suka fito

kwansu da kwarkwata su tarbe shi

kuma ya shawarci su kasance masu

kishin Najeriya domin ba su da wata

kasar bayan ita.

Ya kara da cewa, " ya zama dole

dukkanmu mu hannu hannu wurin

guda domin ciyar da kasar mu gaba

saboda ba mu da wata kasar bayan

wannan."

A baya, Ameachi ya shaidawa 'yan

jam'iyyar da magoya bayansu cewar za

a farfado da layin dogo na yankin

kudu.

Ya ce babban aikin da za muyi shine,

"zamu amince da shimfida layin dogo

daga Fatakwal zuwa Maiduguri wanda

zai wuce Fatakwal zuwa Onitsa har

zuwa Awka.

"Na biyun kuma zai bi ta Fatakwal,

Umuahia, Enugu, Makurdi da Jos."

Amaechi ya ce, "sauya tsarin rabon

arzikin kasa zai yiwu ne idan aka sake

zaben shugaba Muhammadu Buhari

saboda dan kabilar Ibo ya zama

shugaban kasa bayan Buhari ya

kammala wa'adinsa

Thursday, 24 January 2019

Kun San Abin Da Buhari Ya Fadawa Sakkwatawa?



Tawagar yakin neman zaben shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ta isa jihar Sakkwato da ke arewa maso yammacin

kasar a yau Laraba, a ci gaba da neman

kuri’u da shugaban yake yi na neman

wa’adi na biyu.

Ga kadan daga cikin abin da ya fadawa

al’umar jihar Sakkwato kamar yadda

wakilinmu Muratala Faruk Sanyinna ya

aiko mana da rahoto:

Boko Haram: “Cikin ikon Allah, ku ne

shaidu, mun yi iyakar kokarinmu,

kuma a jiya, mutanen Borno sun

tabbata mun ci karfin Boko Haram.

Noma: “Batun arzikin kasa da wadata,

Allah ya taimake mu, damunoni biyu

da suka wuce, sun yi albarka.”

Cin Hanci Da Rashawa: “Batun cin hanci

da rashawa, wannan gwamnatin tana

kokari akan ka’idodin da aka kafa. Na

yi muku alkawarin, ni ba zan ci

amanarku ba, ba kuma zan ga ana cin

amanarku ba in kyale.” Yayin nasa jawabin, Ministan sufuri kuma shugaban gangamin yakin

neman zaben shugaba Buhari, Rotimi Amaechi, ya sha alwashin za a gina layin dogo da zai hade yankunan jihohin Sakkwato, Kebbi da Zamfara.

kalli wasu Zafafan hotunan Fati Yola



 Daga www.hausanet.ml

Zafafan hotunan Fati Yola

Akwai dadi aLadidi abdullahi 'Tubeless' ta yi kira ga maza su rika auren 'yan fim


Daya daga cikin fitattun jaruman nan na

masana'antar shirya fina-finan Hausa na

Kannywood mai fitowa a matsayin uwa

wadda Ladidi Abdullahi amma wadda aka

fi sani da Ladidi Tube less ta yi ikirarin

cewa duk duniya babbu mace mai dadin

aure kamar 'yar fim.

Ladidi ta kara da cewa ita 'yar fim

saboda irin yadda take taka rawa a

cikin fina-finai, tana kara ilimin

zamantakewa irin ta aure sosai a don haka ne ma take kira ga maza su rika

auren 'yan fim din

Kalli wasu zafafan kayatattun hotunan Maryam Yahaya




 Maryam

Yahaya

Kalli wasu zafafan kayatattun hotunan Maryam Yahaya




 Maryam

Yahaya

Na Samu Komai Sauran Abu Daya Amina Amal Umar



1. Amal Umar

-Na Samu Komai Sauran Abu Daya.

2. Shirin fim a 2018: Da dadi, ba dadi!

3.Burin Hairat Abdullahi Zabiya mai

muryar zinari.

4.Karairayin Aliyu Ibrahim Kankara kan

tarihin Shata.

5.2019: ‘Yan takarar da ‘yan fim su ke

so

6.Marin Adam A. Zango saboda gulma!

7.Matsalolin auren ‘yan fim, daga

Zakiyya Ibrahim.

8.Sai yaushe Sadiq Zazzabi zai yi aure?

9. Yaushe Nafisa Abdullahi ta soma

Bilicin?

Wednesday, 23 January 2019

Kalli Wasu Zafafan Kayatattun Hotunan Maryam Yahaya



Sabon photon Maryam yahya Wanda babu dan kwali akanta abindai sai Wanda yagani


Sabon photon Maryam yahya Wanda

babu dan kwali akanta abindai sai Wanda

yagani wow kai wlh kinyi matukar kyau

Ko a dajin Sambisa za'a ajiye akwatin zabe zamu je mu sakawa Buhari kuri'a Inji wani dan jihar Yobe


Wannan wani hoton masoyan shugaban kasa,

Muhammadu Buharine a jihar Yobe inda yaje

yakin neman zabe, jiya, hoton ya dauki hankula

saboda irin sakonnin da mutanen ke dauke dashi

a kan kwalayen da suke rike dasu.

Daya daga cikin kwalayen yace, na yadda da

Buhari fiye da yadda na yarda da kaina.

Dayan kuwa yace, mu 'yan jihar Yobe dole mu

sake zabenka a karo na biyu ko da kuwa a dajin

Sambisa za'a ajiye akwatin zaben

Tuesday, 22 January 2019

Ko a dajin Sambisa za'a ajiye akwatin zabe zamu je mu sakawa Buhari kuri'a Inji wani dan jihar Yobe


Wannan wani hoton masoyan shugaban kasa,

Muhammadu Buharine a jihar Yobe inda yaje

yakin neman zabe, jiya, hoton ya dauki hankula

saboda irin sakonnin da mutanen ke dauke dashi

a kan kwalayen da suke rike dasu.

Daya daga cikin kwalayen yace, na yadda da

Buhari fiye da yadda na yarda da kaina.

Dayan kuwa yace, mu 'yan jihar Yobe dole mu

sake zabenka a karo na biyu ko da kuwa a dajin

Sambisa za'a ajiye akwatin zaben

Kalli Chiroki lokacin da yake karbar tallafin Naira dubu dari biyu da tamanin 280 da aka bashi

Tauraron fina-finan Hausa, Bashir Bala Chiroki

kenan a wannan hoton yayin da ya karbi

gudummuwar Naira dubu 215 da aka tara mai ta

hanyar shafin NorthernHibiscus dake dandalin

Instagram.

Labarin halin da Chiroki yake ciki ya watsune

bayan da aka yi hira dashi a gidan talabijin na

Arewa24 inda yace yanzu sana'ar saida kunu

yake sanadiyyar watsi dashi da masana'antar

fina-finan Hausa tayi.

Tauraro Ali Nuhu dai ya musanta wannan ikirari

na Chiroki inda yace har yanzu ana yi dashi

sannan kuma irin talaucin da ake tunanin

Chirokin ya shiga a zahiri ba haka bane

wata masoyiyar buhari Ta fashe da kuka bayan da taga shugaba Buhari


Wannan wata baiwar Allah ce, da ta fashe da

kuka yayin da ta yi arba da shugaban kasa,

Muhammadu Buhari a gurin yakin neman zabe

da ya je yi a jihar Borno.

Atiku ba Bafulatani bane Miyetti Allah ta bayyana daga inda tsohon mataimakin shugaban kasar ya fito


Miyyeti Allah tace Atiku na amfani da

matsalar yan Fulani wajen yin kamfen

dinsa

- Kungiyar tace tsohon shugaban kasa ba

Bafulatani bane

- An tattaro cewa Atiku yace Buhari ba

Bafulatani bane

Kungiyar Miyetti Allah Kautal Hore

Fulani ta bayyana cewa dan takarar

shugaban kasa na jam’iyyar Peoples

Democratic Party (PDP), Atiku Abubakar

ba Bafulatani bane.

Jaridar Punch ta rahoto cewa Saleh

Alhassan wanda ya kasance babban

sakataren kungiyar na kasa na martani

ne ga ikirarin Atiku na cewa shugaban

kasa Muhammadu Buhari ba Bafulatani

usuli bane.

A wani gangami a igawa, an tattaro

inda Atiku yace: “Bafulatanin usuli ba

zai efa dan uwansa a cikin kangin

talauci ba kamar yadda yake faruwa a

yanzu a karkashin gwamnatin All

Progressives Congress."

Atiku ba Bafulatani bane – Miyetti Allah ta

bayyana daga inda tsohon mataimakin shugaban

kasar ya fito

Alhassan yace don Atiku na yaren

Fulatanci ba yana nufin shi Bafulatani

bane.

Yace: "Batun gaskiya shine, a wurare da

dama a jihar Adamawa, suna yaren

Fulatanci. Don Atiku ya iya Fulatanci ba

yana nufin shi Bafulatani bane.

"Idan ka kalli kirar Atiku, baya dauke da

siffar Bafulatani. Kana kallon Atiku ka

ga dan kabilar Bantu. Ba dan kabilar

Sudan bane.


Monday, 21 January 2019

Mutane ashirin da shida 26 sun mallaki dukiyar rabin al'ummar duniya

Wani rahoton Kungiyar Agaji ta Oxfam ya

bayyana cewa, mutane 26 da ke kan gaba

wajen yawan arziki, sun mallaki

kwatankwacin kadarorin rabin al'ummar

duniya. Oxfam ta bukaci gwamnatocin

kasashe da su tsauwala haraji kan

mawadatan domin rage ratar da ke tsakaninsu

da talakawa.

Sabon rahoton da aka wallafa gabanin taron

tattalin arziki na Davos, ya bayyana cewa,

attajiran da suka mallaki biliyoyin kudi a duniya,

sun samu habbakar duniya da akalla Dala biliyan

2.5 a kowacce rana a shekarar da ta wuce.

Oxfam ta ce, shugaban Kamfanin Amazon, Jeff

Bezos da ya zarce kowa arziki, ya samu

habbakar dukiyarsa da Dala biliyan 112 a bara

kadai, yayin da kungiyar ta ce, kashi daya na

dukiyarsa, shi ne ya yi daidai da kasasfin kudin

kiwon lafiyar kasar Habasha mai yawan al’umma

miliyan 105.

A gefe guda kungiyar ta ce, talakawa biliyan 3.8

sun samu karayar tattalin arziki da akalla kashi

11 cikin shekarar bara, abin da ke nufin cewa,

wannan banbancin da ke tsakanin matalauta da

mawadata ya dada nuna gazawar hukumomi

wajen yaki da talauci a duniya.

Shugabar Oxfam, Winnie Byanyima ta ce,

talakawan duniya sun fusata saboda yadda

matsalar tattalin arzikin ta dabaibaye su.

Kungiyar ta zargi gwamnaton kasashen duniya

da rura matsalar rashin daidaito tsakanin

talakawan da masu hali saboda gazawarsu

wajen samar da kudaden gina al’umma

Atiku Abubakar ya zabo wata jarumar fim domin ta tayashi yakin neman zaben 2019

Atiku ya nada wannan jaruma ce mukamin jami’a mai kula da matasan Nollywood gaba daya, ta yadda zata karkato masa ra’ayin

matasan Nollywood da nufin su bashi goyon baya tare da tallatashi, har sai ya

kai ga nasara a zaben shugaban kasa

Regina

Jarumar mai shekaru goma sha takwas

a rayuwa ce ta sanar da wannan cigaba da ta samu a shafinta na kafar

sadarwar zamani ta Instagram, inda tace tana goyon bayan Atiku dari bisa dari, kuma zata bada duk gudunmuwar data dace don ganin ya samu nasara. “Sunana Regina Daniels, ina alfahari da kasancewata yar Atiku dari bisa dari, na amince da mukamin daya nadani na mai

kula da matasan Nollywood, zan yi aiki tukuru saboda Atiku mutum ne mutunta matasa, kuma yayi alkawarin zai baiwa matasa mukamin ministoci a gwamnatinsa  Najeriya na cikin mawuyacin hali, jama’a na fama da yunwa, lokaci yayi da zamu karkatar da akalar kasar zuwa tudun mun tsira, tun daga Bama har zuwa Bori, Aba zuwa Abuja, Kaura Namoda zuwa Kaduna, lokaci yayi da matasan Najeriya zasu hada kai dani wajen zaban Atiku/Obi a 2019 don kare rayuwarmu  Inji ta

Regina 

na daga cikin fitattun jaruman fina finan Nollywood da suka bayyana goyon bayansu ga tafiyar Atiku Abubakar a shafukan sadarwar zamani, sai dai rahotanni sun tabbatar da cewar masana’antar Kannywood da ta Nollywood ta rabu gida biyu tsakanin yan Atiku da yan Buhari

Siyasar 2019 ta dauki sabon salo Buhari ba bafulatani bane –inji Atiku


Dan takarar shugaban kasa a karkashin inuwar jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari ba asalin bafulatani bane tunda dai baya jin fillanci.

Atiku ya bayyana haka ne yayin

gangamin yakin neman zabensa daya

gudana a garin Dutse, babban birnin jahar Jigawa, inda yace idan ba Buhari cikakken bafulatani ne, da bai jefa mabiyansa cikin halin tsiya da talauci da yan Najeriya ke fama dashi a gwamnatinsa ba

Saye Da Sayarwar Zaratan 'Yan- wasan Kwallon Kafa Na Duniya


James zai cigaba da zama a Bayern Munich har

izuwa karshen kakar bana.


Manchester United, Liverpool suna neman dan

wasan Benfica mai shekaru 21 mai suna Joao

Felix.

Coach din Chelsea wato Maurizio Sarri yace

bazai taba canza salon buga wasansa ba dukda

ya samu rashin nasara a hannun Arsenal. Chelsea da Manchester City suna neman matashin dan wasan Barcelona mai suna Ilaix

Moriba, Coach din Liverpool yace zai iya hakura da sayen yan wasa a January din nan dukda matsalar rauni dan wasu daga cikin yan wasansa suke fuskanta.

Arsenal da Monaco suna neman dan wasan Atletico Madrid mai suna Gelson Martins.


Agent din dan wasan baya na Porto mai suna Eder Militao yace dan wasan bazaije Manchester United a wannan watan ba, kuma idan ma zai bar

Porto din to Spain zai koma.

Shugaban Barcelona wato Josep Maria Bartomeu

ya tafi Amsterdam domin kokarin tattaunawa da

dan wasan tsakiya na Ajax – dan wasan dai an

rawaito yafi sha’awar zuwa zuwa PSG domin

kuwa sune zasu ringa biyansa kudi mai yawa fiye

da Barcelona.


Dan wasan gaba na West Ham wato Andy Carroll

ka iya komawa Tottenham sakamakon rauni da

dan wasan gaban Tottenham din yayi wato Kane.


Ana sa ran cewa Chelsea yau zata kammala

daukan dan wasa Higuain a matsayin aro – shi

kuma dan wasa Emerson zai koma Juventus din.

Matashin dan wasan gaba na Genoa mai suna

Krzysztof Piatek zai koma AC Milan akan kudi

Euro Million 30.


Juventus tana daf da daukan dan wasan baya na

Manchester United mai suna Darmain a matsayin

aro.

Hadiza Gabon ta yi kyau a wadannan hotunan




Tauraruwar fina-finan Hausa, Hadiza Gabon kenan a wadannan hotunan nata da ta sha kyau

tubarkallah, muna mata fatan Alheri