. Kun San Abin Da Buhari Ya Fadawa Sakkwatawa? - hausanet hausanet





Thursday, 24 January 2019

Home › › Kun San Abin Da Buhari Ya Fadawa Sakkwatawa?

Subscribe Our Channel




Tawagar yakin neman zaben shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ta isa jihar Sakkwato da ke arewa maso yammacin

kasar a yau Laraba, a ci gaba da neman

kuri’u da shugaban yake yi na neman

wa’adi na biyu.

Ga kadan daga cikin abin da ya fadawa

al’umar jihar Sakkwato kamar yadda

wakilinmu Muratala Faruk Sanyinna ya

aiko mana da rahoto:

Boko Haram: “Cikin ikon Allah, ku ne

shaidu, mun yi iyakar kokarinmu,

kuma a jiya, mutanen Borno sun

tabbata mun ci karfin Boko Haram.

Noma: “Batun arzikin kasa da wadata,

Allah ya taimake mu, damunoni biyu

da suka wuce, sun yi albarka.”

Cin Hanci Da Rashawa: “Batun cin hanci

da rashawa, wannan gwamnatin tana

kokari akan ka’idodin da aka kafa. Na

yi muku alkawarin, ni ba zan ci

amanarku ba, ba kuma zan ga ana cin

amanarku ba in kyale.” Yayin nasa jawabin, Ministan sufuri kuma shugaban gangamin yakin

neman zaben shugaba Buhari, Rotimi Amaechi, ya sha alwashin za a gina layin dogo da zai hade yankunan jihohin Sakkwato, Kebbi da Zamfara.