. Amaechi ya saka ni a matsala - Buhari - hausanet hausanet





Friday, 25 January 2019

Home › › Amaechi ya saka ni a matsala - Buhari

Subscribe Our Channel



A yau, Alhamis ne shugaba

Muhammadu Buhari ya ce MInistan

Sufuri, Rotimi Amaechi ya jefa shi a

cikin matsala yayin da ya yi alkawarin

gina layin dogo da za ta hade yankin

Kudu maso Gabashin kasar da Arewa.

Shugaba Buhari ya yi wannan jawabin

ne a wurin taron kaddamar da yakin

neman zabensa da akayi a cikin filin

motsa jiki na Nnamdi Azikwe da ke

garin Enugu.

Buhari ya ce abu ne mai wahala

gamsar da majalisar zartarwa na kasa

su amince da ayyukan layin dogo amma

ya ce zai yi iya kokarinsa domin ganin

'yan majalisar sun fahimci

muhimmancin gudanar da aikin.

"Amaechi ya yi muku alkawari amma

ban san yadda zan cika alkawarin ba.

Amma zanyi iya kokari na domin ganin

'yan majalisar zartarwa sun amince da

gudanar da aikin," inji Buhari.

Ya ce ba a gabatar wa Majalisar

Zartarwa alkawarin da Amaechi ya yi

ba inda ya ce zai fi dacewa a bari

Majalisar su amince da aikin kafin a

bayyana wa mutane.

Shugaban kasar ya mika godiyarsa ga

mutanen yankin bisa yadda suka fito

kwansu da kwarkwata su tarbe shi

kuma ya shawarci su kasance masu

kishin Najeriya domin ba su da wata

kasar bayan ita.

Ya kara da cewa, " ya zama dole

dukkanmu mu hannu hannu wurin

guda domin ciyar da kasar mu gaba

saboda ba mu da wata kasar bayan

wannan."

A baya, Ameachi ya shaidawa 'yan

jam'iyyar da magoya bayansu cewar za

a farfado da layin dogo na yankin

kudu.

Ya ce babban aikin da za muyi shine,

"zamu amince da shimfida layin dogo

daga Fatakwal zuwa Maiduguri wanda

zai wuce Fatakwal zuwa Onitsa har

zuwa Awka.

"Na biyun kuma zai bi ta Fatakwal,

Umuahia, Enugu, Makurdi da Jos."

Amaechi ya ce, "sauya tsarin rabon

arzikin kasa zai yiwu ne idan aka sake

zaben shugaba Muhammadu Buhari

saboda dan kabilar Ibo ya zama

shugaban kasa bayan Buhari ya

kammala wa'adinsa