. Portugal za ta kwace lambar yabo mafi girma da ta baiwa Ronaldo - hausanet hausanet





Friday, 25 January 2019

Home › › Portugal za ta kwace lambar yabo mafi girma da ta baiwa Ronaldo

Subscribe Our Channel


Shugaban Portugal Marcelo Rebelo de Sousa,

ya ce gwamnatinsa tana nazari kan yiwuwar

kwace babbar lambar yabo da ta baiwa dan

wasan kasar Cristiano Ronaldo.

Matakin a cewar shugaba Rebelo de Sousa, na

da nasaba da hukuncin biyan tara da kotun

Spain ta yanke kan Ronaldo, bayan samunsa da

laifin kin biyan haraji, yayin da yake wasa a

kungiyar Real Madrid.

A shekarar 2016 Portugal ta karrama Ronaldo

da lambar yabo mafi girma da ake baiwa farar

hula ta ‘Portuguese Order of Merit’ a turance,

bayan taimakawa kasar da ya yi, wajen lashe

gasar cin kofin kasashen nahiyar Turai.

Sai dai a ranar Talatar da ta gabata, wata kotun

Spain ta yanke hukuncin tilasatawa Cristiano

Ronaldo biyan Dala miliyan 3 da dubu 57 saboda

kin biyan makudan kudade na haraji ga

gwamnatin kasar.

Da fari hukuncin kan Ronoldo na daurin

shekaru 2 biyu ne a gidan Yari amma aka

sassauta hukuncin zuwa biyan tarar euro dubu

365 na take, tare da biyan karin euro miliyan 3

da dubu 200