. ka Karanta Abinda Shi'a Babban Darakta Falalu Dorayi Akan Bashar Chiroki - hausanet hausanet





Friday, 25 January 2019

Home › › ka Karanta Abinda Shi'a Babban Darakta Falalu Dorayi Akan Bashar Chiroki

Subscribe Our Channel


Allah shi yake kaddarawa bawa  samu da rashi, wanda Allah ya nufe shi da zama cikin kunci ko rashin wadatar abubuwa da saba rayuwa dasu, ba

kaskanci ba ne face jarraba da kuma

kaddarar Allah akansa.

Mai hankali yasan duniya bala'ice gida

ne na jarrabawa tsakanin wadata da

tsanani.

Ubangiji Yace;

“Kuma za mu jarraba ku da sharri da

alheri a matsayin fitina, kuma gare Mu

kuke komawa.'' (Anbiya:35). Bai

kamata ga mutum idan ya tsinci kansa

a cikin Jarrabawa ta kunci ko talauci

ko dusashewar daukaka ko ciwo ya

zargi wasu mutane ba. Allah yana

jarabtar bawa Sakamakon abin da ya

aikata ga ‘Yan uwansa mutane na

Alfahari, Dagawa da Girman kai. To

shin Ina ma matsayin takawakkali da

yadda kaddara?

Tawakkali ga Allah shine abin bukata

daga ko wane mutum,

a ko wanne hali ya tsinci kansa.

Cikakken tawakkali shin zuciya ta

nutsu ta mika komai ga Allah ta haka

za’a samu alkairi da kariyar daga

sharri.

Babu wanda ya isa ya baka daukaka ko

ya kwaceta sai Allah in dai ka dagara

ga Allah hakikani dogaro, Allah zai

azurtaka kamar yadda yake azurta

tsuntsu da sauran dabbobi.

In gaske ne mutum ya fawwala

lamuransa ga Allah, ya yadda da Allah

shi yake bada daukaka da daukewarta to sai a nisanci Kage, zargi, camfi, da

tazarta masana’antar da Allah ya baka Suna a cikin ta kai aure kai gida kasai

babur. Lallai in da kake yanzu haka

Allah ya so ya ganka

Ubangiji Yace; cikin Qurani

“Kuma Idan Allah ya shafe ka da wata Cuta, babu mai yaye ta, sai shi, idan kuma ya shafe ka da wani alheri, babu mai iya ture falalarsa. Yana samun wanda ya so daga cikin bayinsa da ita,

kuma shi mai gafara ne, mai jin kai