. Manchester City zata iya lashe kofuna 4 a wannan kaka inji Guardiola - hausanet hausanet





Friday, 25 January 2019

Home › › Manchester City zata iya lashe kofuna 4 a wannan kaka inji Guardiola

Subscribe Our Channel


Kocin kungiyar kwallon kafa ta Manchester City Pep Guardiola ya ce abin alfahari ne ya zamana Club din ya yi nasarar lashe kofuna har 4 cikin kaka guda dai dai lokacin da ya ke shirin Komawa wasannin cin kofin FA bayan

takaitaccen hutu. City dai ita ce kungiya daya tilo da ta ke da zarafin iya lashe kofunan Firimiya da FA da kofin League da kuma zakarun Turai la’akari da

matakin da ta ke a kowacce gasa.

Yanzu haka dai City na da tazarar maki 4 ne

kacal tsakaninta da Liverpool da ke saman

Teburi, a bangare guda kuma an ga rawar da ta

ke takawa a gasar ta FA da ma yadda ta ke

shirin tunkarar wasan karshe a gasar League

tsakaninta da Chelsea cikin watan Fabarairu

baya ga gasar zakarun Turai. A gobe asabar ne Manchester City za ta kara da Burnley a zagaye na 4 na wasannin cin

kofin FA