. Mutane ashirin da shida 26 sun mallaki dukiyar rabin al'ummar duniya - hausanet hausanet





Monday, 21 January 2019

Home › › Mutane ashirin da shida 26 sun mallaki dukiyar rabin al'ummar duniya

Subscribe Our Channel


Wani rahoton Kungiyar Agaji ta Oxfam ya

bayyana cewa, mutane 26 da ke kan gaba

wajen yawan arziki, sun mallaki

kwatankwacin kadarorin rabin al'ummar

duniya. Oxfam ta bukaci gwamnatocin

kasashe da su tsauwala haraji kan

mawadatan domin rage ratar da ke tsakaninsu

da talakawa.

Sabon rahoton da aka wallafa gabanin taron

tattalin arziki na Davos, ya bayyana cewa,

attajiran da suka mallaki biliyoyin kudi a duniya,

sun samu habbakar duniya da akalla Dala biliyan

2.5 a kowacce rana a shekarar da ta wuce.

Oxfam ta ce, shugaban Kamfanin Amazon, Jeff

Bezos da ya zarce kowa arziki, ya samu

habbakar dukiyarsa da Dala biliyan 112 a bara

kadai, yayin da kungiyar ta ce, kashi daya na

dukiyarsa, shi ne ya yi daidai da kasasfin kudin

kiwon lafiyar kasar Habasha mai yawan al’umma

miliyan 105.

A gefe guda kungiyar ta ce, talakawa biliyan 3.8

sun samu karayar tattalin arziki da akalla kashi

11 cikin shekarar bara, abin da ke nufin cewa,

wannan banbancin da ke tsakanin matalauta da

mawadata ya dada nuna gazawar hukumomi

wajen yaki da talauci a duniya.

Shugabar Oxfam, Winnie Byanyima ta ce,

talakawan duniya sun fusata saboda yadda

matsalar tattalin arzikin ta dabaibaye su.

Kungiyar ta zargi gwamnaton kasashen duniya

da rura matsalar rashin daidaito tsakanin

talakawan da masu hali saboda gazawarsu

wajen samar da kudaden gina al’umma