. Atiku Abubakar ya zabo wata jarumar fim domin ta tayashi yakin neman zaben 2019 - hausanet hausanet





Monday, 21 January 2019

Home › › Atiku Abubakar ya zabo wata jarumar fim domin ta tayashi yakin neman zaben 2019

Subscribe Our Channel


Atiku ya nada wannan jaruma ce mukamin jami’a mai kula da matasan Nollywood gaba daya, ta yadda zata karkato masa ra’ayin

matasan Nollywood da nufin su bashi goyon baya tare da tallatashi, har sai ya

kai ga nasara a zaben shugaban kasa

Regina

Jarumar mai shekaru goma sha takwas

a rayuwa ce ta sanar da wannan cigaba da ta samu a shafinta na kafar

sadarwar zamani ta Instagram, inda tace tana goyon bayan Atiku dari bisa dari, kuma zata bada duk gudunmuwar data dace don ganin ya samu nasara. “Sunana Regina Daniels, ina alfahari da kasancewata yar Atiku dari bisa dari, na amince da mukamin daya nadani na mai

kula da matasan Nollywood, zan yi aiki tukuru saboda Atiku mutum ne mutunta matasa, kuma yayi alkawarin zai baiwa matasa mukamin ministoci a gwamnatinsa  Najeriya na cikin mawuyacin hali, jama’a na fama da yunwa, lokaci yayi da zamu karkatar da akalar kasar zuwa tudun mun tsira, tun daga Bama har zuwa Bori, Aba zuwa Abuja, Kaura Namoda zuwa Kaduna, lokaci yayi da matasan Najeriya zasu hada kai dani wajen zaban Atiku/Obi a 2019 don kare rayuwarmu  Inji ta

Regina 

na daga cikin fitattun jaruman fina finan Nollywood da suka bayyana goyon bayansu ga tafiyar Atiku Abubakar a shafukan sadarwar zamani, sai dai rahotanni sun tabbatar da cewar masana’antar Kannywood da ta Nollywood ta rabu gida biyu tsakanin yan Atiku da yan Buhari