Shugaban kungiyar “One 2 To 10” mai yiwa shugaba Buhari yakin neman zabe reshen jihar Katsina, Dakta Mannir El-Yakubu, y ace babu gudu, babu ja-da-baya a kan kudirin kungiyar na samar wa da shugaba Buhari kuri’u miliyan 19 a zaben shugaban
kasa na ranar Asabar. Da yake Magana a wurin taron yakin neman zaben shugaba Buhari a jihar Katsina, El-Yakubu, y ace kungiyar su za ta tabbatar da cewar shugaba Buhari ya samu kuri’a miliyan daya daga kowacce jiha daga jihohi 19 da ke fadin arewacin Najeriya.
Ya kara da cewa dandazon jama’ar da su ka halarci taron kamfen din Buhari a jihar Katsina shaida ce da ke nuna cewar mutanen jihar na tare dan su tare da bayyana cewar shugaban kasa
Buhari na da daraja a duk in da ya shiga a duniya. Kazalika, ya bayyana cewar shugaban kungiyar sun a kasa, Dakta Baffa Bichi, bait aba nuna gajiya wa ba a rangadin da kungiyar ta yi na dukkan mazabun da ke jihohin arewa 19 domin nema wa Buhari jama’a.
No comments:
Write Please Share a Your Opinion.