. Kotu ta umurci EFCC ta ci gaba da tsare Babachir Lawal, ba beli - hausanet hausanet





Tuesday, 12 February 2019

Home › › Kotu ta umurci EFCC ta ci gaba da tsare Babachir Lawal, ba beli

Subscribe Our Channel



Wata babbar kotun gwamnatin tarayya ta bayar da umurnin cewa Mr Babachir Lawal, zai ci gaba da zama a hannun hukumar da ke yaki da cin hanci da rashawa EFCC  Kotun ta sanya ranar Laraba, 13 ga watan Fabreru a matsayin ranar da za ta ci gaba da sauraro shari'ar

 Hukumar tana zargin tsohon sakataren gwamnatin tarayyar da aikata laifuka 10 da suka shafi hada baki tare da sama da fadi da kudaden gwamnati

Wata babbar kotun gwamnatin tarayya da ke da zama a Abuja, ta bayar da umurnin cewa tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Mr Babachir Lawal zai ci gaba da zama a hannun hukumar da ke yaki da cin hanci da rashawa da yiwa dukiyar gwamnati zagon kasa (EFCC) Hakan na nufin cewa hukumar EFCC za ta ci gaba da tsare Mr Babachir Lawal, bayan da kotun a ranar Talata ta ki amincewa da bukatar bayar da belinsa Kotun ta sanya ranar Laraba, 13 ga watan Fabreru a matsayin ranar da za ta ci gaba da sauraro shari'ar.