Wata babbar kotun gwamnatin tarayya ta bayar da umurnin cewa Mr Babachir Lawal, zai ci gaba da zama a hannun hukumar da ke yaki da cin hanci da rashawa EFCC Kotun ta sanya ranar Laraba, 13 ga watan Fabreru a matsayin ranar da za ta ci gaba da sauraro shari'ar
Hukumar tana zargin tsohon sakataren gwamnatin tarayyar da aikata laifuka 10 da suka shafi hada baki tare da sama da fadi da kudaden gwamnati
Wata babbar kotun gwamnatin tarayya da ke da zama a Abuja, ta bayar da umurnin cewa tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Mr Babachir Lawal zai ci gaba da zama a hannun hukumar da ke yaki da cin hanci da rashawa da yiwa dukiyar gwamnati zagon kasa (EFCC) Hakan na nufin cewa hukumar EFCC za ta ci gaba da tsare Mr Babachir Lawal, bayan da kotun a ranar Talata ta ki amincewa da bukatar bayar da belinsa Kotun ta sanya ranar Laraba, 13 ga watan Fabreru a matsayin ranar da za ta ci gaba da sauraro shari'ar.
No comments:
Write Please Share a Your Opinion.