Fitaccen jarumin masana’antr shirya fina- finan Hausa (Kannywood), Abba El- Mustapha, ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su san cewar akwai rayuwa bayan zabe, don haka kar su bari siyasa ta raba kan su. El-Mustapha, wanda aka fi sani da
Abba Ruda’ ya yi wannan jan hankali ne a wani rubutaccen sako da ya fitar a shafin sa na sada zumunta (Instagram) yayin hutun krshen mako. Kada ka bari siyasa ta had aka rigima da kowa. Ka yi siyasa cikin mutunci da girmama wa don akwai rayuwa bayan zabe,” a cewar jarumin. Jarumin ya kara yin kira ga ‘yan Najeriya a kan su daina dage wa a kan Lallai sai an bi ra’ayin sun a siyasa.domin kowa da nasa ra’ayin
No comments:
Write Please Share a Your Opinion.