Shahararriyar jarumar nan ta Kannywood wacce
aka dama da ita a lokutan baya, Sadiya
Muhammad Gyale ta yi tsokaci akan abunda ta
sa a gaba bayan barinta masana’antar ta shirya
fina-finai.
A cewar jarumar ta kama sana’a ne gadan-
gadan, inda ta ke saida kayayyaki daban-daban.
Sadiya tace tana saida kayan mata, na maza
dama kayan noma domin tafiyar da al’amuranta
na yau da kullun.
Dandalin Kannywood: Abunda na sa gaba bayan
daina fitowa a fim – Sadiya Gyale
Dandalin Kannywood: Abunda na sa gaba bayan
daina fitowa a fim – Sadiya Gyale
Jarumar ta bayyana hakan ne a wani hira da tayi
da jaridar Leadership Hausa.
KU KARANTA KUMA: Fadar shugaban kasa ta
kare Buhari akan amincewa da bayar da $1bn na
tsaro
Da aka tambayeta kan batun aure, kyakyawar
jarumar tace Insha Allah suna ta addu’a, Allah Ya
kawo miji nagari mafi alheri.
No comments:
Write Please Share a Your Opinion.