Mu-hadu-a-2023: Buhari ne zai lashe zaben 2019 da gagarumin rinjaye - Hon Abdulmumini Jibrin
Damajalisar tarayyar nan mai wakiltar mazabar kananan hukumomin Bebeji da Kiru daga Kano da yanzu haka yake a matsayin korarre daga majalisar Alhaji Abdulmumin Jibrin ya bayyana cewa yanzu kam ta tabbata shugaba Buhari zai lashe zaben 2019 da gagarumin rinjaye. Dan majalisar da ya bayyana hakan a shafin sa na sada zumuntar Tuwita ya Kuma bayyana nasarorin da shugaban Kasar ya samu tare kuma da jam'iyyar adawa marar karfi a matsayin wasu dalilan da za su sa shugaban ya sake Lashe zaben cikin ruwan sanyi |
No comments:
Write Please Share a Your Opinion.